Hausa NewsNews

Matawalle yasa dokan da zata kawo karken ‘yan bindigan a jahar

Gomna matawalle zamfara ya Saka hannu a dokar kisa ga duk Wanda aka kama Yana Satan mutane ko Satan shanu ko fashi ko tsafi a jahar zamfara.

Gomna matawalle yayi wan Nan jawabi ne a Wani takarda da ya Saka hannu a ranar talata inda yace dole wan Nan shine babban matakin da zasu iya dauka saboda kawo karken ‘yan bindigan da suka addaba zamfara.

Zamfara tayi kaurin suna sosai wajen matsalar rashin tsaro a arewacin Nigeria inda yankin zamfara da Katsina suna Daya daga cikin garuruwan da Yan bindigan suka addaba, ta inda a kulum zaka iya Jin ankai hare hare a wan Nan yankuna.

Gomna matawalle yace dukkanin Wani doka da zamu Saka akan wan Nan Yan bindiga mun Saka a baya, amma a yanzu ya zama dole mu kawo karken wan Nan taadanci da yanke hukuncin kisa ga duk Wanda aka kama yanayi ko Kuma Yana temaka musu ko waye shi Kuma ko a Ina yake

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page